News
Wani Jirgin Saman Sojin Najeriya Ya Yi Hatsari A Jihar Kaduna.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wani jirgin sama na sojin Najeriya ya yi hatsari a kauyen Tami da ke yankin Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
Wani mazaunin yankin ya ce jirgin sojin mai saukar ungulu ne, kuma ya yi hatsari ne da misalin karfe 5 na asubar Litinin din nan.
Ka Guji Maimaita Kuskuren Da Buhari Ya yi Na Son Zuciya – Shehu Sani Ya Gargadi Tinubu
Mazauna yankin sun bayyana cewa matukin ya fito daga cikin tarkacen jirgin da ya fado.
Bayan nan sojoji suka yi gaggawar zuwa suka yi wa yankin kawanya tare da fara bincike.
Sojojin sun kuma hana mutane isa wurin da tarkacen jirgin yake.
An ce jirgin yana tsaka da aikin sintiri a yankin ne ya samu matsala, lamarin da ya haddasa faduwarsa.
Kawo yanzu Hedikwatar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ba ta fitar da sanarwar game da lamarin ba.
Kakakin rundunar a Jihar Kaduna, Alaere Eyinimiere Obidake, ya ki daga kiran da muka yi masa domin neman bahasi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
