News
Jami’ar Bayero Ta Dakatar Da Duk Wani Jadawalin Karatu Saboda Zanga-Zanga
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Bayan dogon nazari kan halin da ake ciki a Jihar Kano sakamakon Zanga-Zanga, hukumar gudanarwar Jami’ar Bayero ta bayar da umarnin dakatar da duk wani jadawalin karatu da aka tsara nan take. Da zarar komai ya daidaita, za a ci gaba da duk wasu ayyukan ilimi da na gudanarwa cikin tsari kamar yadda aka shirya.
Cikin wata sanarwar da Lamara Garba, mataimakin maga takarda da harkokin Jama’a, an ba da shawarar ga ɗalibai da mazauna cikin harabar jami’ar da su kasance cikin nutsuwa da bin doka, an yi tanadi mai kyau domin tabbatar da tsaron su.
Rasha Ta Nesanta Kanta Da Masu Ɗaga Tutocin Ƙasarta A Zanga-zangar Nijeriya
Hukumar tana mai yin cikakken shiri musamman don bayar da tsaron rayuka da dukiyoyi, don haka tana jawo hankalin mambobin al’ummar jami’ar da su yi taka-tsan-tsan da yawan fita waje don kauce wa duk wani haɗari mai yiwuwa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
