Connect with us

News

Da Ɗumi-Ɗumi: WAEC Ta Fitar Da Sakamakon Jarabawar WASSCE Ta Shekarar 2024

Published

on

Da Ɗumi ƊumiWAEC ta Fitar Da Sakamakon Jarabawar WASSCE Ta 2024

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar shirya jarabawar kammala sakandire ta Afirka ta Yamma (WAEC) a ranar litinin ta fitar da sakamakon jarabawar kammala makarantun sakandare ta Afirka ta Yamma ta shekarar 2024 ga dalibai.

Hukumar ra WAEC ta tabbatar da hakan a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na X.

Ƴan Siyasa Na Haɗa Kai Da Ma’aikata Wajen Wawure Dukiyar Al’umma – Muhyi Magaji

Hukumar ta sanar da ɗaliban da suka yi jarrabawar da su shiga shafin yanar gizon hukumar na  waecdirect.org don samun sakamakonsu.

“Muna farin cikin sanar da dalibau da suka zauna rubuta jarabawar WASSCE ta ‘shakarar  2024, cewa an fitar da sakamakon a hukumance a yau Litinin, 12 ga watan Agusta, 2024.

“Don samun damar ganin sakamakon, ɗaliban su ziyarci shafin mu na waecdirect.org.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending