News
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabannin A Hukumar DSS Da NIA
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Adeola Oluwatosin Ajayi a mastayin sabon shugaban hukumar ‘yan sandan farin kaya (DSS)
Ajayi zai maye gurbin Yusuf Magaji Bichi wanda shine shugaban hukumar tun lokacin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.
Cinkoson Ababen Hawa Ya Tsayar Da Hanyar Kaduna Zuwa Abuja Cak
Sannan ya naɗa Ambasada Muhammad Muhammad a matsayin shugaban hukumar leƙen asiri na Nijeriya bayan murabus ɗin tsohon shugaban Ahmed Rufai.
Wannan sanarwar ta fito daga bakin mai ba shugaban ƙasa shawara a fannin yaɗa labarai Ajuri Ngelale.
Advertisements
