News
Mutum 2 Sun Mutu A Rushewar Bene Mai Hawa Biyu A Kano
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
An tabbatar da mutuwar mutum biyu, wasu biyu kuma sun tsallake rijiya da baya, a sakamakon rushewar wani bene mai hawa biyu a Jihar Kano.
Da misalin ƙarfe biyu a dare kafin wayewar garin ranar Alhamis ne benen ya rushe da su a unguwar Nomansland da ke Ƙaramar Hukumar Fagge.
Benen ya rushe ne a sakamakon ambaliyar ruwa, kasancewar yana kusa ne da hanyar ruwan.
Benen ya rushe ne a sakamakon ambaliyar da ta biyo bayan ruwan sama kamar da baƙin kwarya na tsawon sa’o’i a cikin daren.
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta sanar da hakan a safiyar Alhamis.
Kakakin hukumar, Samun Abdullahi, ya ce an garzaya da waɗanda aka ceto daga bene d ya rushe zuwa asibiti, inda suke samun kulawa.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
