Connect with us

News

Ana Gudanar Da Zaben Gwamnan Jihar Edo

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

Tun da safiyar yau dubban mutane suka fita zuwa rumfunan zaɓe a faɗin jihar domin kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnan Jihar Edo da ke kudancin Nijeriya.

Advertisement

‘Yan takara 17 ne waɗanda suka haɗa da maza 16 da mace ɗaya ke fafatawa a zaɓen domin neman maye gurbin gwamna mai ci a halin yanzu wato Godwin Obaseki.

Kungiyar Vision Spring Da Tallafin M’G’E Medical Store Sun Yiwa Masu Fama Da Larurar Ido Gwaji Kyauta

Sai dai daga cikin ‘yan takarar 17, mutum uku ne za a iya cewa za su fi fafatawa a tsakaninsu.

Advertisement

‘Yan takarar ukun waɗanda suka fi shahara sun haɗa da Asuerinme Ighodalo na Jam’iyyar PDP sai Monday Okpebholo na Jam’iyyar APC da kuma Olumide Osaigbovo Akpata na Jam’iyyar Labour Party.

A wannan zaɓen wanda ake gudanarwa a ƙananan hukumomi 18 na Jihar Edo, mutum miliyan 2.2 ne suka cancanta su jefa ƙuri’a, kamar yadda hukumar zaɓe ta ƙasa INEC ta tabbatar.

Advertisement

Rahotanni sun tabbatar da jibge jami’an tsaro masu ɗumbin yawa a jihar waɗanda suka haɗa da sojoji da ‘yan sanda da jami’an NSCDC musamman a Benin City babban birnin jihar.

Jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun tabbatar da aika ‘yan sanda 35,000 jihar domin tabbatar da tsaro, haka kuma ‘yan sandan sun tabbatar da aika jirage marasa matuƙa da helikwafta da sauran kayayyakin aiki domin taimakawa a wurin tabbatar da tsaro a yayin zaɓen.

Advertisement

 

TRT Afrika

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending