News
Majalisar Kogi Ta Bukaci Shugaba Tinubu Ya Gaggauta Tsige Shugaban Hukumar EFCC
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Majalisar Dokokin Jihar Kogi ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya gaggauta tsige Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede, wanda ta zarga da kawo ruɗani a batun binciken tsohon gwamnan jihar, Kogi Yahaya Bello.
Majalisar ta zargi hukumar dayin shisshigin kutsawa Gidan Gwamnatin Kogi da ke Abuja, wanda EFCC suka yi harbi a cikin gidan.
Jaridar Puch ta rawaito EFCC ta afka cikin Gidan Saukar Baƙi na Gwamnatin Kogi a Abuja cikin makon jiya, domin kamo Yahaya Bello, wanda Hukumar tayi zargin cewa yana cikin gidan.
To sai dai ‘yan majalisar sun ce EFCC ta keta doka da ta yi harbi a cikin gidan, gwamnati kuma hakan da suka yi, yunƙuri ne na kashe Gwamnan Kogi da ke kan mulki a yanzu haka wato Gwamna Ahmed Ododo.
Kakakin Majalisar Kogi, Aliyu Yusuf, ya ce “abin da EFCC ta yi ya nuna irin yadda hukumar ba ta girmama tafarkin dokokin ƙasa, ta saka siyasa a batun yaƙi da cin hanci da rashawa.
A zaman ta ranar Litinin, majalisar ta yi kira ga Shugaba Tinubu ya gaggauta tsige Shugaban Hukumar EFCC, Olukoyede, “saboda bai ƙware wajen yaƙi da cin hanci da rashawa ba, ya saka siyasa a cikin aikinsa.”
Majalisar ta ce abin da EFCC ta yi a Gidan Gwamnatin Jihar Kogi a Abuja, zai iya lahanta Gwamna Ododo da tsohon gwamnan jihar, Yahaya Bello.
‘Yan Majalisa irin su Akus Lawal, Jacob Olawunmi da kuma Abu Jibril mai wakiltar ƙaramar hukumar Ajaokuta, duk sun nemi a gaggauta gurfanar da Shugaban EFCC Kuma a hukunta shi.
Jibril ya ce Shugaban EFCC da kan sa ya umarci jami’an sa su yi harbi a cikin Gidan Gwamnatin Jihar Kogi a Abuja, inda tsohon gwamnan ya nemi mafaka
Wannan na zuwa ne daidai lokacin da aketa samun sabanin bayanai na cewa tsohon gwamnan Jihar Kogi Yahya Bello ya’kai kansa ga hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin Kasa zagon Kasa inda Hukumar ta musunta cewar tsohon Gwamnan baya hannunta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
