News
Manchester City ta lallasa Manchester United a gasar Firimiya
Daga Muhammad Muhammad Zahraddin
Manchester City ta lallasa Manchester United a gasar Firimiya
Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta casa Manchester United a gasar Firimiya ta kasar Ingila da ci 4-1.
Filin wasa na Etihad ne ya karbi bakuncin wasan da ya gudana a ranar Lahadi 06 ga Maris din 2022.
Manchester United da Manchester City dai na hamayya da juna, wanda hakan ya sa fafatawar ta dauki hankalin magoya bayan kungiyoyi biyun.
Dan wasa Kevin De Bruyne ne ya zura kwallaye biyu a minti na (4′) da (27′)
Kana shima dan wasan kasar Algeria Riyard Mahrez ya zura kwallaye biyu a mintuna na (67′) da (90′)
Sai dai dan wasan Manchester United da kasar Ingila Jadon Sancho ya zura kwallo daya a minti na (21′) da jumulla kungiyarsa tayi rashin nasara da ci 4-1.
Kawo yanzu Manchester City na matakin farko da maki 69 a wasanni 28 da ta buga.
Yayinda kungiyar kwallon kafa ta Manchester United take a mataki na biyar da maki 47.
-
Uncategorized6 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News20 hours ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
