News
Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un :Allah Ya Yiwa Mahaifiyar Gwamnan Jigawa Rasuwa
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Hajiya Maryam Namadi, mahaifiya ga gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, ta rigamu gidan gaskia a safiyar yau Laraba.
Sanarwar Rasuwa ta fito ne ta hannun Babban sakataren yada labarai Hamisu Mohammed Gumel a cikin sanarwa da ya fitar a yau.
Hukumar Karbar Korafe-korafe Ta Kama Jami’an Tsaro Da Ake Zargi Da Badakalar Filaye A Kano
Haka kuma Sanarwar ta ce, za a gudanar da jana’izar ta da karfe 4:30 na yamma a mahaifar su da ke Kafin Hausa, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Advertisements
