News
Ƴan’sanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Dan Yi’Yi Tsafi Da Ita A Facebook
DAGA KABIR BASIRU FULATAN
Rundunar Ƴansandan jihar Kwara sun yi nasarar kama wani saurayi, mai suna Abdulrahman Bello, wanda ake zargi da Kashe budurwarsa Hafsoh Lawal, dalibar da ke shirin kammala karatu a kwalejin Ilimi ta Kwara State College of Education.
Mai magana da yawun ‘yansanda, Toun Ejire-Adeyemi, ne ya tabbatar da kama Abdulrahman Bello mai shekaru 25 a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.
‘Yansanda sun bayyana cewa an fara neman Hafsoh ne bayan mahaifinta Ibrahim A. Lawal ya kai rahoto cewa ta fita halartar bikin suna a ranar 10 ga Fabrairu, 2025, amma ba ta dawo gida ba. Duk ƙoƙarin kiran wayarta ya ci tura.
Bayan bincike ta hanyar fasaha, an gano inda wayarta take, tare da samun gawarta da saurayin ya daddatsa a cikin Durom wanda hakan ya kai ga kama Abdulrahman Bello. Lokacin da aka kama shi, ya amince da laifin kisan Hafsoh da nufin yin sihirin kudi na (oshole/ajoo owo).
Rahotanni sun tabbatar da Hafsa sun hadu da saurayita Abdurrahman ne a kafar sada zumunta ta Facebook wacce suka fara soyayya
Tuni dai aka tura Abdulrahman zuwa sashen binciken manyan laifuka (SCID) Ilorin, domin zurfafa bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Shima mai martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana takaici kan wannan ɗanyen aiki, yana mai cewa “abin baƙin ciki ne, kuma yana da ban tsoro sannan ya bukaci malaman Juma’a dasu Kara dage tsange wajen yiwa Jama’a nasiha.
Ya buƙaci iyaye su ƙara sa ido kan ‘ya’yansu, tare da kula da irin mutanen da suke mu’amala da su.
