Connect with us

News

Kuskure Ne Fara Cin Abinci Tun Daga Gida Kafin Fara Tafiya Ga Mai Ajiye Azumin Ramadan – Sheikh Pantami

Published

on

Sheikh Isa Ali a yayin karatun tafsirin Alƙur'ani da yake gudanarwa, ya bayyana cewa ana iya ajiye azumi a halin tafiya. Amma ba ya halatta a ajiye azumin har sai an kama hanyar tafiyar.
Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Isa Ali Pantami

DAGA YAISR SANI ABDULLAHI 

Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Isa Ali Pantami, ya bayyana cewa ba ya halatta mai azumi ya fara cin abinci tun daga gida kafin fara tafiya a watan Ramadan.

Advertisement

Malamin ya bayyana hakan ne yayin tafsirin Alƙur’ani da yake gudanarwa, inda ya bayyana cewa izinin ajiye azumi a halin tafiya yana farawa ne kawai bayan an fara tafiya.

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Yan Bijilanti 12 Da Yin Garkuwa Da 4 A Zamfara

Ya ce:”Idan mutum yana da niyyar tafiya, ba shi da damar ajiye azumi har sai ya kama hanyar tafiya. Amma idan yana gida, dole ne ya ci gaba da azumi har sai ya fara tafiya.”

Advertisement

Sheikh Pantami ya yi kira ga al’umma da su kiyaye wannan doka, domin kauce wa kuskuren da yawa ke tafkawa a lokacin Ramadan.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending