News
Farfesa Mahmood Yakubu Ya Tabbatar Da Kammala Aiki A Matsayin Shugaban INEC
A bana ne wa’adin Farfesa Mahmood Yakubu zai kare a matsayin shugaban Hukumar Zabe ta Kasa mai zaman kanta (INEC), inda ya fara yin bankwana da abokan aikinsa daga sassa daban-daban na nahiyar Afirka.
Yakubu ya bayyana haka ne yayin wani taro na musamman da shugabannin hukumomin zabe na kasashen ECOWAS (ECONEC) a Banjul, Gambiya, inda ya ce wannan shi ne karo na karshe da zai halarci irin wannan taro a matsayin shugaban INEC.
Ya yi amfani da damar wajen bukatar karin hadin gwiwa tsakanin hukumomin gudanar da zabe a yammacin Afirka domin karfafa dimokuraɗiyya.
Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Abba Kyari Da Wasu Jami’ai Da Ake Zargi.
A baya-bayan nan, an yi ta yada jita-jitar cewa an sauke Yakubu daga mukaminsa, sai dai a makon da ya gabata, ya bayyana a taron mako-mako na shugabannin INEC a Abuja inda ya karyata wannan jita-jita.
Amma a ranar Laraba, jita-jitar ta sake daukar zafi bayan shugaban jam’iyyar LP da tawagarsa sun kai ziyara ofishin INEC kuma suka hadu da mukaddashin shugaban hukumar, Sam Olumekun. Kakakin hukumar, Rotimi Oyekanmi, ya bayyana cewa Yakubu yana wajen taron ECONEC a kasar waje, don haka Olumekun ke rike da mukaddashin shugabanci na wucin gadi.
Yayin jawabi ga takwarorinsa a taron ECONEC, Yakubu ya yi dogon bayani kan ci gaban da aka samu a fannin zabe tun daga shekarar 2017, inda ya bayyana cewa dukkanin kasashen yammacin Afirka suna karkashin mulkin dimokuraɗiyya. Sai dai, ya nuna damuwa da cewa a halin yanzu, kasashe hudu sun koma mulkin soja, yana mai fatan dimokuraɗiyya za ta dawo da karfinta a nahiyar.
Tun bayan bayyana cewa wa’adin Yakubu na gab da karewa, an fara samun ce-ce-ku-ce a fagen siyasa dangane da wanda zai gaje shi da kuma yankin da zai fito. Wasu daga Arewa suna bukatar a bai wa sauran yankuna dama su jagoranci INEC, ba kawai Kudu maso Yamma ba, wanda ke da shugaban kasa a yanzu.
Rahotannin da ke yawo na cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Farfesa Bashiru Olamilekan a matsayin sabon shugaban INEC, sun kara hura wutar muhawarar. Wannan ya haifar da zargin nuna bambancin kabila, musamman daga wasu ‘yan Arewa da ke ganin Tinubu na fifita mutanen yankinsa.
Sai dai Sanata Femi Okurounmu daga yankin Kudu maso Yamma ya kalubalanci wannan ra’ayi, yana mai cewa shugaban kasa na da ikon nadin duk wanda ya dace bisa tsarin doka. Ya kara da cewa tun daga kafuwar hukumar zabe a shekarar 1960, babu dan Kudu maso Yamma da aka taba nada a matsayin shugaban hukumar.
A nasa bangaren, jigon siyasar Arewa, Alhaji Tanko Yakasai, ya jaddada cewa tsarin mulki ya bai wa shugaban kasa ikon nadin shugaban INEC, kuma bai kamata a saka siyasar kabilanci cikin lamarin ba. Ya ce kamar yadda Buhari ya nada Yakubu, ya kamata a bar Tinubu ya yi nadin da ya dace.
Shugaban kungiyar Middle Belt Leaders Forum, Birtus Porgu, ya bayyana ce-ce-ku-cen a matsayin bata lokaci, yana mai cewa kundin tsarin mulki ya bai wa shugaban kasa cikakken ikon zabar wanda zai shugabanci INEC.
Haka kuma, shugaban matasan Arewa, Yerima Shettima, da darakta janar na NCFront, Wale Okunniyi, sun bukaci garambawul ga tsarin zabe da yadda ake nadin shugaban INEC, domin tabbatar da cewa hukumar ba ta kasance karkashin ikon mutum daya ba.
A karshe, kakakin INEC, Rotimi Oyekanmi, ya bayyana cewa tafiyar Yakubu zuwa taron kasa da kasa ce ta sanya Olumekun ke rike da matsayin mukaddashi, ba wai saboda wa’adinsa ya kare ba.
