Connect with us

News

TA’ADDANCI A ZAMFARA: ‘Yan Bindiga Sun Kona Masallacin Juma’a, Asibiti Da Gidaje 

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari garin Biyabiki da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, inda suka kona masallacisn Juma’a, asibitin kula da lafiyar farko da kuma gidaje sama da goma a ranar Asabar da misalin karfe 8 na dare.

Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa harin na iya zama ramuwar gayya daga mabiyan wani sanannen shugaban ‘yan bindiga, Adamu Aliero, bayan hallaka dan uwansa Isuhu Yellow da dansa a wani artabu da jami’an tsaro makonni uku da suka wuce a yankin Keta.

Advertisement

An Kama Mafarauta Huɗu Ƴan Asalin Jihar Kano A Edo

Wani mazaunin garin da ya nemi a boye sunansa saboda tsaro ya shaida cewa: “Ba su kashe ko kama kowa ba, amma sun kona wurare da dama ciki har da masallacin Juma’a da asibitin unguwa. Hakanan sun rusa gidaje akalla goma.”

Mazauna yankin sun bayyana fargabarsu kan yadda hare-haren ke kara ta’azzara tun bayan rasuwar Isuhu Yellow. “Tun bayan mutuwarsa muke fama da hare-hare iri-iri. Muna zargin wannan wani bangare ne na daukar fansa,” in ji wani mazaunin yankin.

Advertisement

Kokarin da aka yi don jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya ci tura, domin bai dauki kiran wayar da aka masa ba.

Wannan hari na baya-bayan nan yana ci gaba da jaddada yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a jihar Zamfara, duk da ayyukan rundunar soji da sauran jami’an tsaro a yankin.

Advertisement

 

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending