News
Madarasatul Tarbiyatul Aulad Academy Za Ta Yi Bikin Saukar Dalibai 23 A Karo Na Biyu
A ranar Asabar, 3 ga watan Mayu 2025, Madarasatul Tarbiyatul Aulad Academy da ke Sheka Sabuwar Abuja za ta gudanar da bikin saukar karatun Al-Qur’ani mai girma na dalibai 23, karo na biyu, karkashin jagorancin Alhaji Shafi’u Ya’u.
An shirya gudanar da bikin cikin yanayi na farin ciki da annashuwa, inda iyaye, malamai da manyan baki za su hallara domin taya daliban murnar wannan gagarumar nasara. Ana sa ran babban taron zai samu halartar manyan baki da dama, ciki har da uban taro Alhaji Abubakar Musa Zakari (Dagacin Sheka), da uban makaranta, Malam Yusuf Limamun Sheka.
Daga cikin fitattun bakin da za su halarci bikin akwai:
Alhaji Abdullah Maliya Gidan Kudi
Nura Ahmad Gwaski
Oga Sogira Farm Center
Alhaji Haruna Engineer
Malam Yakubu Director, da sauransu.
Haka kuma, wasu daga cikin manyan bakin na musamman da ake sa ran ganinsu sun hada da:
Alhaji Shafi’u Ya’u (Sarki)
Alhaji Bashir Ali Mai Agogo (Magajin Garin Bawura, Kano)
Hon. Usaman Abubakar Larba
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da sauransu.
Shugabannin kungiyar iyaye da malamai (PTA) na makarantar, karkashin jagorancin Malam Auwal Abubakar, sun nuna cikakken goyon baya ga cigaban makarantar da dalibanta. Malaman makaranta maza da mata, ciki har da Malam Abubakar Ya’u Muhd (Director), Malam Abdullah Yusuf, Malama Zainab Isah (Assistant Director), da Malama Mai’muna Umar Ibrahim (Head Teacher), za su halarci taron cikin cikakken shiri.
Bikin, wanda zai gudana a Sheka/Abuja, layin Malam Sheikh, a gidan Bulon Alhaji Ya’u, zai fara da misalin karfe 9:00 na safe. Za a kaddamar da sabuwar kalandar makarantar a wajen taron, tare da gudanar da addu’o’i na musamman domin fatan alheri ga daliban da suka sauke karatu da kuma cigaban makarantar.
An tanadi tsare-tsare na musamman domin tabbatar da gudanar da taron cikin tsari da zaman lafiya, inda za a rufe shi da addu’o’in albarka ga makarantar da dukkan masu ruwa da tsaki.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
