Connect with us

News

‎Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Gurin Shagalin Auren Yan Bindiga A Zamfara

Published

on

Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto 

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta kai wani hari ta sama kan wani taron biki da ake zargin na ‘yan bindiga ne, a tsaunukan Asaula da ke cikin ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.

‎Rahotanni daga yankin sun tabbatar da cewa an kai harin ne da misalin ƙarfe 4:00 na yamma ranar Talata, lokacin da ‘yan bindigar suka hallara domin bikin aure, wanda ya haɗa mayaka daga jihohin Zamfara da Katsina.

Advertisement

EFCC Ta Gurfanar da Jami’an Haraji Biyar da Ma’aikacin Banki A Kotu Bisa Zargin Wawure Naira Biliyan 1.2 A Katsina

‎Wata majiya mai tushe daga Zagazola Makama, wata kafar da ke bibiyar al’amuran tsaro a yankin Arewa maso Yamma da Tafkin Chadi, ta ce jirgin yaki ya samu nasarar hallaka wasu daga cikin ‘yan bindigar, yayin da wasu da dama suka jikkata.

‎Bikin, wanda aka ce ya tara manyan ‘yan bindiga daga sassa daban-daban na Zamfara da Katsina, ya kasance wani babban taro ne da harin ya tarwatsa.

Advertisement

Operation Fansar Ƴan Bindiga, wanda rundunar soji ta ƙaddamar a farkon wannan shekarar, na ci gaba da kai hare-hare kan sansanonin ‘yan bindiga da wuraren ɓoyarsu a jihohin Zamfara, Katsina, Kebbi da Sokoto.

‎Kakakin rundunar sojin sama bai fitar da sanarwar hukuma a hukumance ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Advertisement

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending