Connect with us

News

Mun Yi Kuskure’: WAEC Ta Fadi Abin Da Ya Jawo Dalibai Suka Fadi Jarabawar 2025

Published

on

WAEC Ta Sanar Da Sabon Tsarin Gyara Jarrabawar Da Mutum Ya Fadi Ba Sai Ya Yi Jiran Shekara Daya Ba

Hukumar WAEC ta tabbatar da cewa ta samu kuskure a sakamakon jarabawar SSCE na 2025 da ta fitar a farkon mako.

Sabbin bayanai sun nuna cewa yanzu dalibai 1,239,884 (kashi 62.9%) ne suka samu nasara a darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi, maimakon kashi 38.32% da aka sanar da farko.

Advertisement

Gwamnatin Kano za ta kashe Naira Biliyan 14.8 domin gudanar da manyan ayyuka

Shugaban WAEC a Najeriya, Dr. Amos Dangut, ya ce an samu matsala wajen buga tambayoyin Turanci na “objective” inda aka yi amfani da mabuɗin amsa mara daidai, wanda ya shafi daliban da suka yi jarabawar a takarda kawai.

An gyara kuskuren kuma sabbin sakamakon suna samuwa a shafin hukumar www.waecdirect.org.

Advertisement

Cikin waɗanda suka yi nasara akwai 582,065 maza da 657,819 mata.

Duk da haka, an samu raguwar wadanda suka yi nasara a bana da kashi 9.16% idan aka kwatanta da sakamakon 2024.

Advertisement

WAEC ta nemi afuwar dalibai, iyaye da malamai, tare da alkawarin cewa za ta ɗauki matakan hana irin wannan kuskure a nan gaba.

 

Advertisement

WIKKI TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending