Connect with us

News

NNPP Ta Kori Abdulmumin Jibrin Kofa Daga Jam’iyya

Published

on

FB IMG 1757170167130

Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) reshen Jihar Kano ta sanar da koriwar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa, bisa zargin aikata zagon ƙasa ga jam’iyya da kuma rashin biyan kuɗin jam’iyya.

Shugaban NNPP a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya bayyana haka yayin da yake ganawa da ’yan jarida a ranar Asabar, inda ya ce wannan hukunci ya biyo bayan fitowar Kofa a kafafen watsa labarai yana sukar jam’iyya da shugabanninta.

Advertisement

KAMFANONI 91: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayar Da Matatun Man Fetur Da Filayen Jirgin Sama Biyar Ga ‘Yan Kasuwa

Dungurawa ya ce an kafa kwamitin sulhu domin tattaunawa da Kofa bayan bayyana ra’ayinsa a Channels Television, amma daga bisani ya sake fitowa ya kara sukar jam’iyyar, abin da ya tabbatar musu cewa ya “kusa karya doka.”

“Maimaikon tattaunawa, sai ya ci gaba da yi mana adawa, har ma ya bayyana biyayya ga waje da jam’iyya. Shi ya sa muka kori shi, domin babu wani ƙarin ƙima da zai kawo,” in ji Dungurawa.

Advertisement

Shugaban ya kuma ce Kofa ya gaza biyan kuɗin da dokar jam’iyya ta wajabta, tare da barazanar cewa za su gurfanar da shi a kotu domin karɓar kuɗin.

Haka kuma, ya ce nasarar Kofa a zabe ba ta samo asali daga ƙarfinsa na siyasa ba, illa kawai goyon bayan jam’iyya da kuma tasirin tafiyar Kwankwasiyya a ƙarƙashin jagorancin Rabiu Musa Kwankwaso.

Advertisement

Dangane da rade-radin cewa Kofa zai koma jam’iyyar APC, Dungurawa ya ce hakan ba zai kawo illa ga NNPP ba, domin siyasa hadin kai ce, kuma Kwankwasiyya na nan daram tana tare da Kwankwaso.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending