Connect with us

News

‎An Kama Wata Mata Bisa Zargin Kashe ’Ya’yanta Biyu

Published

on

1758622702522

Wata mata mai shekaru 43 ta shiga hannun ’yan sanda a ƙasar Ingila bisa zargin kashe ’ya’yanta guda biyu a cikin gidansu da ke kan titin Corporation Street a garin Stafford.

‎Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da safiyar Asabar da misalin ƙarfe 7:30 na safe, bayan da ma’aikatan asibiti suka kira ’yan sanda don neman taimako. Da isar su wurin, sai suka tarar da yaran biyu sun mutu.

Advertisement

‎Shugabannin Kafofin Yada Labarai A Kano Sun Bukaci Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe ‎

‎Rundunar ’yan sandan Staffordshire ta tabbatar da cewa an kama matar bisa zargin kisan kai, kuma tana tsare a hannunsu domin ci gaba da bincike.

‎Har yanzu ba a bayyana shekarun yaran ba, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano musabbabin mutuwar su.

Advertisement

‎Jami’ar dake  kula da binciken, Det. Insp. Kirsty Oldfield, ta yi kira ga jama’a da su guji yada jita-jita ko yin zato, domin hakan na iya kawo cikas ga bincike da kuma ƙara raɗaɗi ga iyalan yaran.

Advertisement

 

DAILY MAIL 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending