Connect with us

News

‎Sojan Najeriya Ya Kashe Kansa Bayan Ya Halaka Matarsa

Published

on

‎Wani sojan Najeriya mai suna Akenleye Femi da ke aiki a bataliya ta 221 a barikin Wawa da ke karamar hukumar Borgu a jihar Nija ya halaka kansa bayan ya kashe mai dakinsa.

‎Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025, inda ya jefa mazauna barikin cikin tashin hankali da mamaki kan abin da ya iya haifar da hakan.

Advertisement

Manoman Rake A Kano Sun Yi Asarar Sama Da Naira Biliyan 2

‎Mai rikon mukamin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji ta 22, kaftin Stephen Nwankwo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa marigayin yana aiki a bataliya ta 221 da ke barikin Wawa kafin rasuwarsa.

‎Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike domin gano ainihin abin da ya haddasa wannan mummunan lamari.

Advertisement

 

Advertisement

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending