Connect with us

News

Jirgin Ƙasa Ya Faɗi Kwanaki 4 Kacal Bayan An Shafe Watanni Ana Gyare-gyare A Najeriya  ‎

Published

on

images 23 1

Hukumar Jiragen Ƙasa ta Ƙasa (NRC) ta sake dakatar da zirga-zirgar jiragen ƙasa a layin Warri–Itakpe, bayan wani hatsari da ya faru da yammacin Asabar, inda wasu daga cikin tirelolin jirgin suka faɗi.

‎Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:30 na yamma, a daidai kilomita 212+8m da ke kusa da Agbor, a Jihar Delta. Wannan na zuwa ne kwanaki huɗu kacal bayan an dawo da zirga-zirgar jiragen a layin, bayan watanni ana gyare-gyare.

Advertisement

Shugaba Tinubu Zai Gana Da Trump Kan Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya 

‎Layin Warri–Itakpe, wanda ke da tsawon sama da kilomita 300, yana ɗaya daga cikin manyan sabbin layukan jirgin ƙasa na zamani a Najeriya, bayan na Lagos–Ibadan da Abuja–Kaduna.

‎Shugaban hukumar NRC, Injiniya Kayode Opeifa, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce binciken farko ya nuna cewa lalata layin dogo (track vandalism) ne ake zargi da haddasa hatsarin.

Advertisement

‎A cewarsa, “Dukkan fasinjojin da ke cikin jirgin an kwashe su lafiya zuwa Agbor, kuma babu wanda ya ji rauni.”

‎Hukumar ta ce an fara bincike don gano musabbabin lamarin da kuma waɗanda ke da hannu a cikin yiwuwar lalata layin.

Advertisement

‎Sai dai har yanzu NRC ba ta bayyana lokacin da za a sake dawo da zirga-zirgar jiragen a layin ba.

 

Advertisement

PLATINUM POST NEWS

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending