News
Gwamnatin Kwara Ta Rufe Makarantu A Kananan Hukumomi 4
Gwamnatin Jihar Kwara ta umurci rufe dukkan makarantu a kananan hukumomi huɗu saboda karuwar hare-haren ƴan ta’adda a kwanakin baya-bayan nan.
A Bokungi, karamar hukumar Edu, an kashe mutane uku yayin harin ranar Laraba. Wannan lamari ya biyo bayan harin da aka kai cocin Eruku a karamar hukumar Ekiti, inda mutane biyu suka mutu, tare da sace wasu 30.
Shugaba Tinubu Ya Umurci Ministan Tsaro Ya Tare A Kebbi Har Sai An Ceto Dalibai 25 Da Aka Sace
Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakan tsaro a makarantu, ciki har da makarantu masu ɗakin kwana a Irepodun, domin kare ɗalibai daga barayi da ke iya amfani da su a matsayin kariya daga jami’an tsaro. Kuma za a ci gaba da rufe makarantu har sai an tabbatar da tsaro.
Kafin yanzu ‘yan bindiga sun kai hari makarantar GGCSS Maga a Kebbi, inda suka kashe jami’i ɗaya suka sace ɗalibai 25.
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News14 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
