Connect with us

News

Gwamnatin Kwara Ta Rufe Makarantu A Kananan Hukumomi 4

Published

on

IMG 20210611 223159

Gwamnatin Jihar Kwara ta umurci rufe dukkan makarantu a kananan hukumomi huɗu saboda karuwar hare-haren ƴan ta’adda a kwanakin baya-bayan nan.

A Bokungi, karamar hukumar Edu, an kashe mutane uku yayin harin ranar Laraba. Wannan lamari ya biyo bayan harin da aka kai cocin Eruku a karamar hukumar Ekiti, inda mutane biyu suka mutu, tare da sace wasu 30.

Advertisement

Shugaba Tinubu Ya Umurci Ministan Tsaro Ya Tare A Kebbi Har Sai An Ceto Dalibai 25 Da Aka Sace

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakan tsaro a makarantu, ciki har da makarantu masu ɗakin kwana a Irepodun, domin kare ɗalibai daga barayi da ke iya amfani da su a matsayin kariya daga jami’an tsaro. Kuma za a ci gaba da rufe makarantu har sai an tabbatar da tsaro.

Kafin yanzu ‘yan bindiga sun kai hari makarantar GGCSS Maga a Kebbi, inda suka kashe jami’i ɗaya suka sace ɗalibai 25.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending