News
Kotun Koli Ta Soke Afuwar Da Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Maryam Sanda
Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke afuwar da Shugaba Bola Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, wacce aka yanke wa hukuncin kisa ta hanyar rataya a shekarar 2020 saboda kashe mijinta, Bilyaminu Bello.
A hukuncin da ta yanke a ranar Jumma’a a babban birnin ƙasar Abuja, Kotun Kolin ta sake tabbatar da hukuncin kisa ta hanyar rataya a kan Maryam Sanda.
Kotun Koli Ta Soke Afuwar Da Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Maryam Sanda
A watan Oktoba ne Shugaba Tinubu ya yi was Maryam afuwa ta hanyar sassauta mata hukuncin daga na kisa zuwa na zaman gida yari na shekaru 12 a bisa dalilai na tausayawa.
Alkali Moore Adumein wanda ya jagoranci yanke hukuncin ya ce
ba daidai ba ne Shugaban Kasa ya nemi yin amfani da ikon yin afuwa a kan wata shari’ar kisan kai da aka aikata, wadda ake jiran hukuncin ƙarar da aka ɗaukaka a kanta.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News7 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
