News
Sarkin Jinkan Hausawan Afrika ya yi Allah-wadai da kashe matar aure da ’ya’yanta 6 a Kano
Sarkin Jinkan Hausawan Afrika, Ambasada Ibrahim Ali Ibrahim (Abba Alra-iwas), ya yi Allah-wadai da kisan matar aure da ’ya’yanta shida a Jihar Kano.
An kashe Fatima Abubakar mai shekaru 35, tare da ’ya’yanta a gidansu da ke Dorayi Gidan Kwari a ranar Juma’a.
Shugaban Limaman Ilorin Sheikh Muhammad Bashir Saliu Ya Rasu Yana Da Shekaru 75
A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Ambasada Ibrahim Ali Ibrahim ya bayyana lamarin a matsayin abun tashin hankali, kuma ya ce lamarin ya taɓa zuciyar al’ummar Kano.
“Na shiga matuƙar damuwa da girgiza bisa kisan gillar da aka yi wa wata uwa da ’ya’yanta shida a Kano.
“Wannan mugun aiki bai tsaya kan waɗannan mutane ba, ya karya tasirinmu na zaman lafiya da girmama rayuwar ɗan Adam,” in ji shi.
Sarkin Jinkan ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayiyar da sauran waɗanda lamarin ya shafa, tare da yin addu’a ga mamatan.
“Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalan mamatan, da al’ummar Dorayi da Chiranchi, da kuma ɗaukacin al’ummar Jihar Kano.
“Allah Ya gafarta musu, Ya bai wa iyalansu haƙuri da juriyar jure wannan babban rashi,” in ji shu.
Ya kuma yi kira ga gwamnati, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da shugabanni da su haɗa kai wajen kare rayuka da hana aukuwar irin wannan lamari a nan gaba.
