News
Cutar Lassa Ta Yi Ajalin Mutum 31 —NCDC
Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa NCDC ta ce mutum 31 ne suka mutu sakamakon zazzabin Lassa a cikin makonni biyar kacal, a cewar sabon rahoton da ta fitar a ranar Litinin.
Rahoton ya nuna cewa mutum 754 ne ake zargin sun kamu da cutar inda aka tabbatar da cewa 165 suna ɗauke da cutar.
Daga cikin waɗanda suka kamu akwai ma’aikatan lafiya tara.
A cewar rahoton, jihohi tara sun riga sun samu aƙalla mutum ɗaya da aka tabbatar ya kamu a ƙananan hukumomi 33.
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Rigakafin Shanu Miliyan 1.5 Don Dakile Cutar CBPP
Kashi 92 na dukkan waɗanda aka tabbatar sun kamu sun fito ne daga jihohin Bauchi da Ondo da Taraba da Edo da Plateau yayin da sauran kashi takwas suka fito daga wasu jihohi huɗu.
Zazzabin Lassa cuta ce mai tsanani wadda kwayar cutar Lassa ke haddasawa, kuma tana daga cikin cututtukan zubar jini masu haɗari da ke iya sa mace-mace idan ba a gano ta da wuri ba ko a samu kulawar gaggawa ba.
