Connect with us

News

Cutar Lassa Ta Yi Ajalin Mutum 31 —NCDC

Published

on

Zazzabin Lassa Cutar ta yi Ajalin Mutum 118 A Cikin Watanni Uku

Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa NCDC ta ce mutum 31 ne suka mutu sakamakon zazzabin Lassa a cikin makonni biyar kacal, a cewar sabon rahoton da ta fitar a ranar Litinin.

Rahoton ya nuna cewa mutum 754 ne ake zargin sun kamu da cutar inda aka tabbatar da cewa 165 suna ɗauke da cutar.

Advertisement

Daga cikin waɗanda suka kamu akwai ma’aikatan lafiya tara.

A cewar rahoton, jihohi tara sun riga sun samu aƙalla mutum ɗaya da aka tabbatar ya kamu a ƙananan hukumomi 33.

Advertisement

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Rigakafin Shanu Miliyan 1.5 Don Dakile Cutar CBPP ‎

Kashi 92 na dukkan waɗanda aka tabbatar sun kamu sun fito ne daga jihohin Bauchi da Ondo da Taraba da Edo da Plateau yayin da sauran kashi takwas suka fito daga wasu jihohi huɗu.

Advertisement

Zazzabin Lassa cuta ce mai tsanani wadda kwayar cutar Lassa ke haddasawa, kuma tana daga cikin cututtukan zubar jini masu haɗari da ke iya sa mace-mace idan ba a gano ta da wuri ba ko a samu kulawar gaggawa ba.

 

Advertisement

 

BBC HAUSA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending