Connect with us

News

‎ Faɗan Daba Ya Yi Ajalin Mutum Daya Tare Da Jikkata Su A Kano

Published

on

Fadan Daba Ya Haifar Da Zaman Dardar A Unguwanne Da Dama A Cikin Kano
Advertisements
ads

Mutum ɗaya ya rasu, wasu uku kuma sun ji rauni mai tsanani sakamakon rikicin da ya barke tsakanin ƙungiyoyin ’yan daba biyu a Jihar Kano, rahoton jami’an tsaro ya nuna.

‎Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na dare a yankin Ja’en, Unguwar Lalle, bayan wani yunƙurin sulhu tsakanin ɓangarorin biyu ya gaza, in ji masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, a shafinsa na X.

Shugaba Tinubu Ya Mayar Da Hankali Kan Zaɓen 2027 Yanzu, Ya Manta Da Batun Tsaro Da Walwalar Jama’a  —Ndume

‎Wani mazaunin yankin ya kira ’yansanda domin neman agaji. Jami’an tsaron sun garzaya wurin cikin hanzari, inda suka daƙile rikicin kuma suka dawo da zaman lafiya.

‎An kama shugabannin ƙungiyoyin biyu da ake zargi, wato Abubakar Abdullahi mai shekaru 22 daga Sabuwar Madina da Abubakar Bello, wanda aka fi sani da Babuji, mai shekaru 18 daga Unguwar Lalle.

‎A sakamakon rikicin, mutane uku sun ji rauni mai tsanani, inda aka kai su Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad domin samun kulawa. Ɗaya daga cikinsu, Aliyu Abdullahi mai shekaru 22, wanda ya samu rauni a wuya, ya rasu daga baya, yayin da sauran biyun ke ci gaba da jinya.

Advertisement

‎Bayan haka, jami’an ’yansanda sun kai samame inda suka sake kama wasu mutane takwas da ake zargin da hannu a rikicin. An kuma ƙwato makamai kamar adda, takobi da wasu kayan tsafe-tsafe daga hannunsu.

‎Hukumomin tsaro sun ce suna ci gaba da bincike don gano musabbabin rikicin, tare da tabbatar da cewa za a hukunta duk masu hannu a ciki. Ana sa ran karin bayani zai fito nan gaba.

‎Lamarin ya sake jaddada damuwar al’umma kan yawaitar rikice-rikicen ’yan daba a Kano, inda ake kira ga hukumomi da su ƙara tsaurara matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending