Politics
Peter Obi, Seyi Makinde sun halarci taron Kwankwaso
Babban ɗan siyasar nan na Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasar na Jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabiu Kwankwaso, ranar Lahadi ya karɓi baƙuncin takwarorinsa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP, Peter Obi da Gwamnan Jihar Oyo Seyi Makinde.
Da yake jawabi a wajen gangamin magoya bayan Kwankwaso, Peter Obi ya ce ya kai wa jagoran Kwankwasiyya ziyara ce domin yin gaisuwar Sallah da kuma nuna muhimmancin Kwankwaso a siyasar Nijeriya. Shi ma Seyi Makinde ya jinjina wa Kwankwaso.
HAWAN NASARAWA:Gwamnan Kano Ya Musanta Zargin Yin Watsi Da Sarki Sanusi II
Kwankwaso ya miƙa godiya bisa ziyarar tare da bayyana muhimmancin haɗin kai domin ci gaban Nijeriya.
Masana harkokin siyasa na ganin wannan ziyara na da alaƙa da fafutukar da ‘yan siyasar suke yi wajen ganin sun kawar da Jam’iyyar APC daga mulki a zaɓen 2027 mai zuwa.
-
News18 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
