Connect with us

Sports

Ruftawar Gini A Kano: Ana Fargabar Mutane Takwas Sun Mutu A Ghari

Published

on

IMG 20260325 162743 048

Ana fargabar cewa mutane akalla takwas ne suka rasa rayukansu sakamakon ruftawar wani gini a garin Ridawa da ke ƙaramar hukumar Ghari a jihar Kano.

Rahotanni daga majiyar Premier Radio sun ce lamarin ya faru ne a wani lokaci da ba a tantance ba, inda ginin ya rufta dauke da mutane a ciki.

Advertisement

An haifi jarirai sama da 36,000 a Kano cikin watanni 9 — Gwamnatin Tarayya 

A cewar majiyoyin yankin, ana ci gaba da aikin ceto domin gano wadanda suka makale a karkashin baraguzan ginin, yayin da aka fara tono wasu gawarwaki.

Advertisement

Har zuwa yanzu, ba a fitar da cikakken bayani daga hukumomi kan musabbabin ruftawar ginin ba, sai dai ana sa ran za a gudanar da bincike domin gano hakikanin abin da ya haddasa lamarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending