News
Jami’an ‘Yansanda Sun Cafke Wani Mai Safarar Makamai A Kano
Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta ce ta samu nasarar kama wani da ake zargi da dillancin makamai tare da ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda uku a hannunsa.
Kakakin rundunar na jihar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.
Mbappe Ba Zai Buga Wa Madrid Wasan El Clasico Ba
Kiyawa ya ce jami’ansu sun yi nasarar cafke wanda ake zargin yayin wani samame da suka kai unguwar Dandinshe da ke Ƙaramar Hukumar Dala.
Sanarwar ta ce an kama wanda ake zargi mai suna Umar Danladi Usman, mai shekaru 35, mazaunin Kurna Layin Masallacin a cikin wata mota ƙirar Honda Accord.
Sanarwar ta ƙara da cewa yayin tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa cewa ya taho da bindigogin ne daga Ƙaramar Hukumar Dutsin-Ma ta Jihar Katsina.
