News
Yadda Aka Gano Gawar Wata Mata A Bandakin Coci
An gano gawar wata mata mai suna Blessing Ayebe a cikin bandakin wata coci da ke unguwar Ikot Ansa a birnin Calabar, hedikwatar jihar Cross River, lamarin da ya jefa al’umma cikin jimami.
Rahotanni sun nuna cewa marigayiyar ta halarci ibada a cocin Presbyterian Church, Ikot Ansa Parish a ranar 28 ga watan Yuni, amma ba ta koma gida bayan an kammala taron ba, abin da ya sa iyalanta suka fara neman ta.
An Caka Wa Wani Mutum Wuƙa Har Lahira Yayin Da Suke Gardama
Bayan kwana guda ana nemanta, an gano gawarta a cikin bandakin cocin da misalin ƙarfe 9:00 na dare a ranar 29 ga watan Yuni, kamar yadda majiyoyi daga iyalanta suka bayyana.
‘Yarta, Peace Minka Ayebe, ta kai rahoton lamarin ofishin ‘yan sanda na Federal Housing Police Station bayan ɗan uwanta, Saviour Ayebe, ya sanar da ita gano gawar.
Daga nan ne aka kai gawar zuwa ɗakin adana gawarwaki na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Calabar (UCTH), inda za a gudanar da binciken likitoci domin gano ainihin musabbabin mutuwarta.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Cross River, ASP Eitokpah Sunday Akata, ya ce binciken farko da aka gudanar bai gano wata alamar tashin hankali ko raunuka a jikin marigayiyar ba.
Ya ƙara da cewa har yanzu ba a kama ko gano wanda ake zargi ba, domin babu wata shaida da ke nuna cewa an aikata laifi.
-
News7 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized3 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
