News
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Kotun Tafi-da-Gidanka Kan Masu Laifin Miyagun Ƙwayoyi
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da shirin kafa Kotun Tafi-da-Gidanka domin gaggauta sauraren shari’o’in da suka shafi miyagun ƙwayoyi da sauran laifukan zamantakewa a jihar.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar.
Shugaba Tinubu Ya Ba Da Umarnin Binciken Meta Da X Kan Amfani Da Labaran Najeriya
Sanarwar ta ce kafa kotun zai taimaka wajen hanzarta gudanar da shari’a, tabbatar da adalci cikin lokaci, da kuma ƙarfafa bin doka da oda. Ta kuma ce matakin zai zama darasi ga masu aikata irin waɗannan laifuka.
A cewar sanarwar, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ci gaba da yaƙi da matsalar miyagun ƙwayoyi, wadda ke yin illa ga al’ummar jihar, musamman matasa.
Gwamnan ya kuma umarci kwamitin kar-ta-kwana da gwamnatin jihar ta kafa kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ya ƙara ƙaimi tare da haɗa kai da hukumomin da abin ya shafa domin tabbatar da nasarar yaƙin da ake yi da shaye-shaye da sauran laifukan da ke da alaƙa da miyagun ƙwayoyi..
-
News7 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized3 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
