News
Ku Fara Harbe Yan Bindiga Kafin Karbar Umarni — Ministan Tsaro Christopher Musa Ga Dakarun Soji
Ku Fara Harbe Yan Bindiga Kafin Karbar Umarni — Ministan Tsaro Christopher Musa Ga Dakarun Soji
Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya umarci jami’an tsaro da ke fafatawa da ’yan ta’adda da ’yan bindiga da kada su yi jinkirin ɗaukar mataki idan suka ci karo da masu ɗauke da makamai.
Ya ce duk jami’in da aka tura aiki amma ya ƙi fuskantar ’yan ta’adda ko ’yan bindiga da sunan yana jiran umarni, za a ɗauke shi tamkar yana taimaka wa maƙiya.
Mazauna Dorayi Karama Sun Roƙi Gwamnatin Kano Ta Kawo Musu Ɗauki Kan Matsalar Ambaliyar Ruwa
Christopher Musa ya bayyana hakan ne a birnin Sokoto yayin ƙaddamar da motocin sulke da sauran kayan aikin tsaro da gwamnatin jihar ta saya domin ƙarfafa yaƙi da matsalar rashin tsaro.
Ya jaddada cewa duk jami’in da aka tura bakin aiki yana da ikon kare kansa da kuma rayukan al’umma, don haka bai kamata ya jira wani sabon umarni kafin ya fuskanci ’yan bindiga ko ’yan ta’adda ba idan sun bayyana.
Ministan ya kuma buƙaci jami’an tsaron su yi amfani da sabbin kayan aikin yadda ya kamata, yana mai cewa gwamnati ta kashe kuɗaɗe masu yawa wajen samar da su domin ƙarfafa yaƙi da rashin tsaro a sassan ƙasar.
-
News2 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News3 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News3 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
