News
Wani Mutum Ya Hallaka Matarsa Har Lahira Saboda Ta Ƙi Dafa Abinci
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta kama wani mutum mai suna Musbahu Amadu, mai shekara 30, bisa zargin dukan matarsa har ta mutu a unguwar Yahaya da ke Agyaragu, Ƙaramar Hukumar Obi ta jihar.
Kakakin rundunar, SP Ramhan Nansel, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.
Jami’an NDLEA Sun Cafke ‘Yar Afirka Ta Kudu Da Hodar Iblis Filin Jirgin Sama A Abuja
Ya ce ana zargin Musbahu ya lakada wa matarsa mai shekara 20 duka ne bayan wata saɓani da ya shiga tsakaninsu, wanda ake zargin ya samo asali ne bayan matar ta ƙi dafa masa abinci.
A cewarsa, bayan samun rahoton lamarin a Ofishin ’Yan Sanda na Agyaragu, jami’ai suka garzaya wurin tare da kama wanda ake zargin.
Nansel ya ce yayin da ake yi masa tambayoyi, Musbahu ya amsa cewa ya aikata hakan ne cikin fushi, inda ya bayyana cewa gardamar da ta shiga tsakaninsu ta rikide zuwa faɗa, wanda daga bisani ya yi sanadin mutuwar matar.
Ya ce ma’auratan sun yi shekara shida da aure, kuma sun bar yara biyu, ɗa namiji da ɗiya mace.
Sanarwar ta ce Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, CP Shetima Jauro Mohammed, ya ba da umarnin a miƙa shari’ar zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Lafia domin gudanar da cikakken bincike.
-
News4 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News2 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
