News
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana Talata, 1 ga Satumba, 2026, a matsayin ranar hutu domin bai wa mazauna jihar damar gudanar da bikin Takutaha, wata muhimmiyar al’ada ta addini da ake gudanarwa duk shekara.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Ma’aikatar Kafa Dokoki da Ayyukan Gwamnati, Abba A. Danguguwa, ya sanya wa hannu a madadin Shugaban Ma’aikatan Jihar.
“Ba Za Mu Bayar Da Ko Taku Daya Na Kasa Ba Don Yin Burtali Ga Fulani Makiyaya” —Gwamnan Jihar Benue
Sanarwar ta ce ranar hutun ta yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal, 1448 bayan hijira, inda ta ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya amince da ayyana ranar a matsayin hutu.
Gwamnatin ta bayyana Takutaha a matsayin muhimmiyar al’ada mai alaka da addini da tarihi, wadda ke da matukar muhimmanci ga al’ummar Kano tare da kasancewa wani bangare na tarihin Musulunci na jihar.
Ta bukaci ma’aikatan gwamnati da su yi amfani da ranar wajen addu’o’i da neman gafara, tare da rokon Allah Ya tabbatar da zaman lafiya, hadin kai, kwanciyar hankali da ci gaba a Kano da Najeriya baki daya.
Sanarwar ta umurci shugabannin ma’aikatu da hukumomi da su tabbatar da bin umarnin, sai dai ta ce ma’aikatan da ke kula da muhimman ayyuka za su ci gaba da aiki kamar yadda tsarin hukumominsu ya tanada.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
