News
Amarya Ta Rataye Kanta A Zariya Saboda Auren Dole
Daga maryam bashir musa
Al’ummar unguwar Tudun Muntsira da ke Cikaji a Karamar Hukumar Sabon Garin Zariya a Jihar Kaduna sun cika da alhinin yadda wata amarya ta rataye kanta a unguwar.
A ranar Juma’a 29 ga watan Afirilun 2022 da misalin karfe 6.:00 na yamma ne dai labari ya cika unguwar cewar wata matar aure mai suna Sanayya Muhammad nai shekara 16 da a unguwar ta kashe kanta ta hanyar rataya.
Bayanan da Aminiya ta samu shi ne wai an daura mata aure ne da angon nata mai suna Isa Jibrin mai shekara 35 wanda ta ce sam ba ta son shi.
Amaryar dai ’yar asalin garin Nasarawan Doya ce da ke Karamar Hukumar Makarfi da ke Jihar ta Kaduna.
Wani jami’in dan sanda wanda da shi ne aka je inda amaryar ta rataye kanta ya ce sun tarar da ita a mace.
Kazalika, ya ce sun same ta a wani yanayi mara kyan gani, inda nan take suka dauki gawar suka kai ta asibiti domin fadada bincike.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
