News
Gwamnan Ekiti Kayode Fayemi ya ƙaddamar da takarar shugaban ƙasa a APC
Daga yasir sani abdullahi
Gwamnan Jihar Ekiti a kudancin Najeriya, Kayode Fayemi, ya ƙaddamar da takarar neman shugabancin ƙasar a ƙarƙashin jam’iyya mai mulki ta APC a babban zaɓe na 2023.
Fayemi wanda shi ne shugaban Ƙungiyar Gwamnoni ta Najeriya, ya ce zai tabbatar da “kyakkyawan shugabanci da haɗin kan ƙasa” idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa.
Gwamnan zai kara da sauran ‘yan takara a A:PC da suka haɗa da Bola Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo waɗanda suka fito daga shiyya ɗaya ta Kudu maso Yamma. Kazalika akwai Gwamnan Kogi Yahaya Bello, da Gwamnan Ebonyi David Umahi, da sauransu.
APC ta sanya ranar 30 ga watan Mayu zuwa 1 ga watan Yuni don gudanar da zaɓukan fid da gwani tsakanin ‘yan takarar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
