News
An sace mutane ‘da dama’ a hanyar Kaduna zuwa Abuja
Daga yasir sani Abdullah
Rahotanni daga Najeriya na cewa masu garkuwa da mutane sun sace mutane da dama a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a ranar Talata.
Wani wanda ya shaida lamarin ya bayyana wa BBC cewa lamarin ya faru ne a garin Katari da misalin 4:30 na yammaci.
‘Yaran da ke fama da yunwa na ci gaba da karuwa’
Ya bayyana cewa akwai motoci da dama waɗanda suna ajiye a kan ɓangaren zuwa Kaduna da ɓangaren dawowa da aka yi awon gaba da masu motocin.
Ya kuma ce bayan faruwar lamarin jami’an tsaro masu ɗumbin yawa sun isa wurin domin kai ɗauki.
BBC ta tuntuɓi gwamnatin Jihar Kaduna da kuma rundunar ƴan sadan Najeriya reshen Kaduna domin jin ƙarin bayani, sai dai dukansu ba su ɗaga wayoyinmu ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
