News
Ƴan sanda sun kashe ƴan bindiga 6 bayan daƙile wani hari a Katsina
Daga kabiru basiru fulatan
Jami’an ƴan sanda a jihar Katsina, sunyi nasarar daƙile wani harin ƴan ta’adda a ƙauyukan Dabaibayawa da kuma Ɗantakiri dake ƙarƙashin ƙananan hukumomin Batagarawa da Dutsinma na jihar.
Kotu ta ƙi ba da belin Nnamdi Kanu
A yayin daƙile harin, jami’an ƴan sandan sun yi nasarar ƙwato shanun sata su 86 da tumaki tare da awaki 101.
Kakakin Rundunar Ƴan Sandan Jihar, SP Gambo Isah ya sanar da haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.
Ya ce da yawa daga cikin ƴan ta’addan sun ranta a na kare bayan musayar wuta da jami’an tsaron ƴan sandan a inda suka jikkata sakamakon harbin bindiga.
Ya zuwa yanzu dai, ana ci gaba da gudanar da ran gadi a dazukan dake maƙwabtaka da inda al’amarin ya faru domin chafke ko kuma gano gawarwakin ƴan ta’addan da suka tsere da raunuka daban-daban tare da makaman da suke tu’ammali da su.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
