News
Mun Aminta da zabin da Allah yayi akanmu, kalaman Madaki bayan ya rasa tikitin takara a NNPP
Daga muhammad Muhammad Ibrahim
Tsohon Dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Dala daga jihar Kano, kuma wanda ya yiwa jam’iyar PDP takarar Sanatan Kano ta tsakiya a zaben 2019, Aliyu Sani Madaki, ya bayyana cewa ya karbi hukuncin baiwa Sanata Malam Ibrahim Shekarau takarar Sanatan Kano ta tsakiya, dukda shi yake neman kujerar a karkashin jam’iyyar NNPP.
A yau ne dai akayi bikin karbar tsohon gwamna Shekarau zuwa NNPP bayan ya fice daga APC, wanda kuma yayin taron ne, jagoran NNPP na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya mikawa Shekarau fom din takarar Sanata, abinda ke nuni da cewar Madaki ya rasa wannan tikiti.
Bayan faruwar hakan, Madaki ya bayyana biyayyarsa ga wannan hukunci, ya kuma fitar da sanarwa a shafinsa na Facebook yana mai godiya ga Allah da kuma masoya da magoya bayansa bisa kaunar da suka nuna masa akan takarar da ya nema ta Sanata, dukda bai samu ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
