Connect with us

News

An Haramta Acaba A Wasu Sassan Birnin Legas ‘Har Abada’

Published

on

Daga Maryam basiru fulatan 

 

 

 

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da haramta sana’ar acaba a Kananan Hukumomi shida na Jihar har abada.

Gwamnan ya sanar da haramcin ne bayan taron da ya yi da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a Jihar a ranar Laraba.

Advertisement

Kwankwaso ya fitar da sunayen ƴan takararar NNPP na maslaha a Kano

Babajide ya a ce haramcin ya shafi Kanana Hukumomin Ikeja da Surulere xa Eti-Osa da Lagos Mainland da Lagos Island da kuma Apapa.

Ya ce haramci ne na har abada, inda ya bukaci ’yan sanda su tabbatar ana bin umarnin yadda ya kamata.

Daukar matakin dai ba ya rasa nasaba da kisan wani matashin mawaki da ake zargin ’yan acaba sun yi inda suka kone gawarsa saboda wata takaddama kan Naira 100 a ranar Alhamis din da ta gabata.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending