News
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya ce nan ba da jimawa ba za a shirya taron tattaunawa na addini a jihar
Daga Maryam Bashir Musa
Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin Sarkin Kano a gidan gwamnati.
Gwamnan ya taya Sarkin murnar karramawar da shugaban kasar Senegal da lamba mafi girma a kasar Senegal.
Ya kuma yi amfani da damarsa wajen taya shi murnar nada shi a matsayin Khalifan Tijjaniyya a Najeriya.
Ganduje ya kuma yaba da gudummawar da majalisar masarautu ke baiwa jihar wajen inganta tsaro domin zaman lafiya ya cigaba da wanzuwa a jihar.
Dr Ganduje, ya yi kira ga al’ummar kasar nan da su yi koyi da dabi’ar son zaman lafiya da fahimtar juna.
A nasa bangaren, mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bayyana cewa ya ga ya dace ya zo kai tsaye domin nuna wa Gwamna lambar yabo da aka ba shi a kasar Senegal.
Yace lambar yabon da aka bashi is a tabbas wani mataki ne da zai karfafa dankon zumuncin kasashen biyu.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
