News
Kudan Zuma Sun Sanadiyyar Mutuwar Wani Yaro Dan Shekara 13 A Jihar Kano
Daga Khadija abdullahi muhmd
Wasu gungun kudan zuma sun kai hari tare da yin sanadiyyar rasa ran wani yaro dan shekara 13 mai suna Ismail Hussaini a kauyen Yanoko dake karamar hukumar Tofa a jihar Kano.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis a makarantar Firamare ta Nomadic ta Yanoko yayin da dalibai ke cikin azuzuwansu.
Dagacin kauyen Yanoko, Habibu Bello ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa an garzaya da wanda abin ya shafa zuwa asibiti inda ya rasu a lokacin da ake kula da lafiyarsa.
Sunusi Bature Dawakintofa, wanda na kusa da marigayin ne, ya shaida wa manema labarai cewa, an kai wa mamacin harin ne biyo bayan kasa guduwa da ya yi saboda cutar da ya ke fama da ita a sakamakon ciwon sikila.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
