News
Kuma Dai: EFCC ta sake gano wata Biliyan 90 da akanta Janar na kasa ya sata wanda yanzu yawan kudin da ake zargin ya sata sun kai Biliyan 170
Daga Maryam bashir musa
A yayin da ake bincikensa kan zargin satar Biliyan 80, Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta EFCC ta sake gano wata Biliyan 90 da ake zargin Akanta janar na kasa, Ahmad Idris ya sata.
A yanzu yawan kudaden da ake zarginsa da ssta sun kai jimullar Naira Biliyan 170 kenan.
Tuni dai Ahmad Idris ya fara fallasa wasu manya-manyan jami’an gwamnati da yace suna da hanni a cikin wannan gagarumar satar.
An yi gobara a gidan Sheikh Ahmad Gumi da ke Kaduna
Akwai babban sakarare da yanzu haka ake bincikensa sannan kuma akwai Minista da shima ake kokarin kamashi kan wannan lamarin.
Sau 80 EFCC na gayyatar Ahmad Idris yana kin amsa gayyarar kamin daga baya ta kamashi da tsiya-tsiya.
Ko da a jiya sai da aka kama tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari kan hannu a satar wadannan makudan kudade.
Rahotanni dai sun ce, Ahmad Idris ya amsa cewa zai dawo da wasu kudaden da ya sace.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
