News
Dakarun MJTF sun hallaka ‘Yan ta’adda sama da 800 a Tafkin Chadi
Daga muslim yunus Abdullah
Sojojin hadakar da ke karkashin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga Najeriya da Nijar da kuma Kamaru sun samu nasarar kashe mayakan ISWAP fiye da 100.
Ƙarancin dakon man fetur ne ya haifar da wahalarsa a ƙasa — IPMAN
Sojojin hadakar da ke karkashin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga Najeriya da Nijar da kuma Kamaru sun samu nasarar kashe mayakan ISWAP fiye da 100.
Rundunar Sojin hadin gwuiwa dake yaki da Yan ta’adda a Yankin Tafkin Chadi ta sanar da kashe mayakan Boko Haram sama da 800 a cikin watanni biyu da suka gabata a tsibirin dake tsakanin kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.
Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito wani rahotan rundunar na cewar tsakanin ranar 28 ga watan Maris zuwa 4 ga watan Yuni, hadin gwuiwan sojojin sun gudanar da samamen hadin kai a Tsibirin dake Tafkin Chadin da kuma kauyukan sa inda suka kashe tarin mayakan boko haram da na ISWAP.
Rahotan ya bayyana samun gagarumar nasara a cikin samamen da suka yi wanda ya kai ga hallaka mutane 805 da kama ko lalata motocin su 44 da babura 22 da kuma tarin kanana da manyan makamai.
Sanarwar tace akalla sojoji 3,000 suka shiga aikin samamen ta kasa da ruwa da kuma sama wanda ya kunshi sojojin kasashen 4 na Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi inda suka kwashe kwanaki 45 suna yi.
Rahotan yace sojojin sun kwace tarin makamai da bama bama bayan gano inda ake sarrafa su, yayin da wasu sojojin Nijar kusan 20 suka samu raunuka sakamakon tashin abin fashewar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
