News
Rikici Ya Barke Tsakanin Shugaban APC Na Jihar Kano Da Jami’an Tsaro A Taron APC
Daga mujahid danlami garba
An dakatar da jefa kuri’a a zaben fid-da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC bayan barkewar wata takaddama tsakanin shugaban jam’iyyar na Jihar Kano, Abdullahi Abbas da jami’an tsaro a zauren taron.
Hatsaniyar ta tashi ne kan zargin magudi a yayin da daliget suke jefa kuri’a a zauren taron da ke gudana a Abuja.
Ƙarancin dakon man fetur ne ya haifar da wahalarsa a ƙasa — IPMAN
Daga baya kwamitin gudanar da zaben fitar da dan takarar ya shawo kan rikcin.
Sai dai kuma ya umarci duk wasu jami’an jam’iyyar da ke sanye da shudin riga su bar wurin da aka ware domin jefa kuri’a.
Daga bisani aka ci gaba da jefa kuri’a da aka fara da daliget din Jihar Legas tun da misalin karfe 2 na dare.
Jihar Kano na da daliget 127 da suka jefa kuri’a a zaben da ke gudana a safiyar ranar Laraba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
