News
Zaben 2023: Kwankwaso ya ce suna tattaunawa da Peter Obi
Daga.Muhammad Muhammad Zahraddin
Dan takara shugaban Najeriya na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya ce yana tattaunaa da takwaransa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi domin yiwuwar hada gwiwa a zaben 2023.
Ya bayyana haka ne a tattaunaarsa da BBC Hausa.
A cewarsa “gaskiya muna magana da shi Peter Obi, ko kuma ma in ce kwamiti yana aiki domin ya duba dukkan abin da ya kamata (kan hada gwiwa da shi), kuma abokai da ‘yan uwa suna zuwa suna yi mana magana kan batun.”
Tsohon gwamnan na Jihar Kano ya ce hada gwiwarsu tana da muhimmanci musamman ganin cewa jam’iyyun APC da PDP ba su tsayar da dan takarar mataimakin shugaban kasa daga yankin kabilar Igbo ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
