Connect with us

News

Mutum 59 sun rasu a India da Bangladesh sakamakon ambaliya da tsawa

Published

on

Daga Muhammad Zahraddin Muhammad

Mamakon ruwan saman da ake tafkawa ya janyo ambaliyar ruwa, da zaftarewar ƙasa, da tsawa mai ƙarfin gaske, tare da asarar rayukan mutum 59 a ƙasashen Bangladesh da India.

Masu aikin ceto, sun duƙufa neman mutanen da suka maƙale a ɗaukacin yankunan ƙasashen da lamarin ya shafa, domin kai su tudun mun tsira.

Yawancin waɗanda suka mutu a Bangladesh, tsawa ce ta faɗa musu.

An dakatar da tashi da saukar jiragen sama, yayin da aka soke jiragen kasa da manyan motocin bas da ke sufuri a manyan tituna.

Masu hasashen yanayi sun yi gargaɗin lamarin zai ƙara munanan, saboda ana sa ran zubar ruwan saman da aka daɗe ba a gani ba cikin kwanaki masu zuwa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending