Connect with us

News

Wani mutum ya kona matarsa a jihar Ogun

Published

on

Babban Sufeton 'yan-sandan Najeriya Usman Alkali

Daga Muhammad Muhammad zahraddin 

 

Advertisement

 

‘Yan-sanda sun ce shi ma mijin ya rasu bayan an kama shiImage caption: ‘Yan-sanda sun ce shi ma mijin ya rasu bayan an kama shi

Advertisement

Abubuwan da suka haddasa tsadar takin zamani a Najeriya

Wani mutum a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya, Ponle Adebanjo, ya kona matarsa, Lateefat, abin da ya kai ga mutuwarta saboda ta gudu ta bar shi a kan yawan dukanta da yake yi.

Advertisement

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar a yankin Otun-Akute da ke jihar ta Ogun.

Advertisement

 

Kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar , DSP Abimbola Oyeyemi, wanda ya tabbatar da lamarin ya ce, a ranar Asabar da daddare ne mijin ya bi matar zuwa wani gida da ta koma a unguwarsu, ya tarar da ita tana sallah, ya kwara mata fetur ya cinna mata wuta.

Advertisement

 

A sanarwara da kakakin ‘yan sandan ya fitar ya ce, ganin haka ya sa ita ma matar ta kama mijin nata ta rike don su kone tare, har sai da mutane suka zo aka shiga tsakani.

Advertisement

 

Kakakin ya ce bayan an garzaya da matar asitbiti ne likita ya tabbatar ta rasu, shi ma kuma mijin daga baya ya rasu kamar yadda sanarwar ta tabbatar, bayan ‘yan sanda sun kama shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending