Connect with us

Sports

Southampton Ta Sayi Dan Wasan Najeriya Joe Aribo

Published

on

Daga Kabiru basiru fulatan 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kungiyar kwallon kafar Southampton da ke gasar Firimiyar Ingila ta rattaba hannu kan kwantaragin shekaru hudu da dan wasan Najeriya, Joe Aribo.

Advertisement

Dalilin Da Ban Zabi Kirista A Matsayin Abokin Takara Ba —Tinubu

Sanarwar da mahukuntan kulob din Southampton suka fitar a ranar Asabar ta ce sun cefano dan wasan tsakiyar ne daga kungiyar Rangers ta Scotland.

Advertisement

Kawo yanzu kungiyoyin kwallon kafa na Rangers da Southampton ba su bayyana kudin da aka yi ciniki dan wasan ba, amma wasu jaridu a Burtaniya na cewa kudaden sun haura Dala 7,000.

Aribo mai shekaru 25 da aka haifa a birnin Landan ya nuna bajinta a zamansa na Rangers, inda a wasanni 150 ya zura kwallaye 26 sannan ya taimaka wa kulob din lashe kofin babbar gasar kwallon kafar Scotland.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending