Connect with us

News

Dalilin da ya sa APC ta sha kashi a zaben gwamnan jihar Osun

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Tsohon mai bai wa gwamnan Osun shawara kan ƙabilu mazauna jihar, Muhammad Bashir, ya bayyana dalilai na siyasa da suka sa jam’iyyar APC mai mulki ta fadi a zaɓen gwamnan jihar.

Advertisements
Advertisements

A wata hira da BBC Alh. Bashir wanda limami ne kuma jami’i a gwamnatin tsohon Gwamna Rauf Aregbesola, ya ce rikicin cikin gida ne ya kayar da jam’iyyar tasu.

Ya ƙara da cewa kusan kashi 90 cikin 100 na mutanensu PDP suka zaɓa, saboda gwamnatin Gboyega Oyetola “ta yi watsi da su”.

ya ci gaba da cewa “Makomarmu yanzu ita ce mu shiga taitayinmu, yanzu abin da muka faɗa wa shugabanni suka ƙi ji yanzu za a koma a sake shiri,” in ji shi.

Advertisements
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending