News
Mu na da man fetur isashshe domin amfanin ƴan ƙasa — NNPC
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Kamfanin Man Fetur na Ƙasa, NNPC, ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa, yana da isashshen man fetur don biyan bukatun ‘yan Najeriya.
Garba Muhammad, mai magana da yawun NNPC ne ya bayar da wannan tabbacin a wata sanarwa da ya fitar a jiya Laraba.
Muhammad ya shawarci jama’a da kada su riƙa sayen man fetur don gudun ƙarancin sa kuma su yi watsi da duk wata jita-jita da ke nuna akasin haka.
“La’akari da dokokin da ake da su a kasar, kamfanin NNPC ya himmatu matuka wajen tabbatar da tsaron makamashin kasar,” in ji Shugaban NNPC.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
